Peter Okoye na kungiyar mawakan P-Square ya ce ,Najeriya tana da kabilu biyu ne kawai, wadanda a cewarsa talakawa ne da masu hannu da shuni.
Shahararren Tauraron mawakin, wanda ke goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jamâiyyar Labour, Peter Obi, ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter.
A cewar shafin na twitter, kasawar talakan da ya samu hadin kai da fafutukar ganin an samar da shugabanci na gari, ya sanya su zama bayi ga âyan tsirarun attajiran Najeriya.
Ya yi kira ga âyan Najeriya musamman wadanda suka cancanci kada kuriâa da su yanke hukunci mai kyau yayin kada kuriâa a babban zabe mai zuwa.
Ya rubuta cewa, âKabila biyu ne kawai muke da su a Najeriya, TALAKAWA da ARZIKI. Talakawa sun fi yawa yayin da masu kudi ba su da yawa amma masu hannu da shuni sun yi nasarar sanya talaka a cikin bautar dawwama domin talaka ya ki hada kai ya yi yaki don kwato musu yanci. Zaben 2023 Ku Zabe Cikin Hikima # ObiDatti023â.