fidelitybank

‘Yan Najeriya ku kiyayi shan magungunan kara karfin maza – NAFDAC

Date:

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) ta gargadi ‘yan Najeriya da su daina amfani da abubuwan kara kuzari da a ka fi sani da aphrodisiac, domin burge abokan zamansu mata, inda ta jaddada cewa shan irin wadannan abubuwan na iya haifar da shanyewar jiki ko kuma mutuwa kwatsam.

Gargadin ya zo ne a daidai lokacin da NAFDAC ta bayyana cewa hukumar ta kama jabun magunguna da haramtattun magunguna da a ka haramta na Naira biliyan 3 da kuma kayayyakin abinci marasa kyau da hukumar ta kama a kwanan baya a harabar kasuwar ta Legas.

Ta kara da cewar, akalla tireloli 20 na irin wadannan haramtattun kayayyaki su ka kwashe su, kuma jami’an hukumar na ci gaba da bincike domin tabbatar da doka karkashin jagorancin Kingsley Ejiofor.

Ya ce wasu daga cikin magungunan da a ka kame a harabar baje kolin kasuwanci na kara kuzari ne.

Hukumar ta kuma gargadi ‘yan Najeriya da su rika lura da abin da su ke ci, inda ta bayyana cewa rashin kulawa na iya yin illa ga lafiyarsu.

Darakta Janar, Farfesa Mojisola Adeyeye, ta ba da wannan gargadi a cikin sakonta na Kirsimeti da na sabuwar shekara ga ’yan Najeriya, inda ta koka kan yadda a ke amfani da kwayoyi masu kara kuzari da a ka fi sani da ‘manpower’ a harshen gida, a kasuwannin Najeriya.

A cewar Adeyeye, galibin magungunan da ke kara kuzari ba su da rijista da NAFDAC.

A cikin wata sanarwa da mai ba da shawara kan harkokin yada labarai na NAFDAC, Sayo Akintola, ya fitar a Legas ranar Lahadi, Adeyeye ya koka da cewa maza da yawa sun mutu ta hanyar amfani da kwayoyi masu kara kuzari kuma ‘yan uwansu za su dora alhakin mutuwarsu a kan wasu bokaye masu gaskiya a kauyen.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp