fidelitybank

‘Yan Najeriya ku kiyayi shan magungunan kara karfin maza – NAFDAC

Date:

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) ta gargadi ‘yan Najeriya da su daina amfani da abubuwan kara kuzari da a ka fi sani da aphrodisiac, domin burge abokan zamansu mata, inda ta jaddada cewa shan irin wadannan abubuwan na iya haifar da shanyewar jiki ko kuma mutuwa kwatsam.

Gargadin ya zo ne a daidai lokacin da NAFDAC ta bayyana cewa hukumar ta kama jabun magunguna da haramtattun magunguna da a ka haramta na Naira biliyan 3 da kuma kayayyakin abinci marasa kyau da hukumar ta kama a kwanan baya a harabar kasuwar ta Legas.

Ta kara da cewar, akalla tireloli 20 na irin wadannan haramtattun kayayyaki su ka kwashe su, kuma jami’an hukumar na ci gaba da bincike domin tabbatar da doka karkashin jagorancin Kingsley Ejiofor.

Ya ce wasu daga cikin magungunan da a ka kame a harabar baje kolin kasuwanci na kara kuzari ne.

Hukumar ta kuma gargadi ‘yan Najeriya da su rika lura da abin da su ke ci, inda ta bayyana cewa rashin kulawa na iya yin illa ga lafiyarsu.

Darakta Janar, Farfesa Mojisola Adeyeye, ta ba da wannan gargadi a cikin sakonta na Kirsimeti da na sabuwar shekara ga ’yan Najeriya, inda ta koka kan yadda a ke amfani da kwayoyi masu kara kuzari da a ka fi sani da ‘manpower’ a harshen gida, a kasuwannin Najeriya.

A cewar Adeyeye, galibin magungunan da ke kara kuzari ba su da rijista da NAFDAC.

A cikin wata sanarwa da mai ba da shawara kan harkokin yada labarai na NAFDAC, Sayo Akintola, ya fitar a Legas ranar Lahadi, Adeyeye ya koka da cewa maza da yawa sun mutu ta hanyar amfani da kwayoyi masu kara kuzari kuma ‘yan uwansu za su dora alhakin mutuwarsu a kan wasu bokaye masu gaskiya a kauyen.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp