fidelitybank

‘Yan Najeriya ku kiyayi shan magungunan kara karfin maza – NAFDAC

Date:

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) ta gargadi ‘yan Najeriya da su daina amfani da abubuwan kara kuzari da a ka fi sani da aphrodisiac, domin burge abokan zamansu mata, inda ta jaddada cewa shan irin wadannan abubuwan na iya haifar da shanyewar jiki ko kuma mutuwa kwatsam.

Gargadin ya zo ne a daidai lokacin da NAFDAC ta bayyana cewa hukumar ta kama jabun magunguna da haramtattun magunguna da a ka haramta na Naira biliyan 3 da kuma kayayyakin abinci marasa kyau da hukumar ta kama a kwanan baya a harabar kasuwar ta Legas.

Ta kara da cewar, akalla tireloli 20 na irin wadannan haramtattun kayayyaki su ka kwashe su, kuma jami’an hukumar na ci gaba da bincike domin tabbatar da doka karkashin jagorancin Kingsley Ejiofor.

Ya ce wasu daga cikin magungunan da a ka kame a harabar baje kolin kasuwanci na kara kuzari ne.

Hukumar ta kuma gargadi ‘yan Najeriya da su rika lura da abin da su ke ci, inda ta bayyana cewa rashin kulawa na iya yin illa ga lafiyarsu.

Darakta Janar, Farfesa Mojisola Adeyeye, ta ba da wannan gargadi a cikin sakonta na Kirsimeti da na sabuwar shekara ga ’yan Najeriya, inda ta koka kan yadda a ke amfani da kwayoyi masu kara kuzari da a ka fi sani da ‘manpower’ a harshen gida, a kasuwannin Najeriya.

A cewar Adeyeye, galibin magungunan da ke kara kuzari ba su da rijista da NAFDAC.

A cikin wata sanarwa da mai ba da shawara kan harkokin yada labarai na NAFDAC, Sayo Akintola, ya fitar a Legas ranar Lahadi, Adeyeye ya koka da cewa maza da yawa sun mutu ta hanyar amfani da kwayoyi masu kara kuzari kuma ‘yan uwansu za su dora alhakin mutuwarsu a kan wasu bokaye masu gaskiya a kauyen.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...
X whatsapp