fidelitybank

‘Yan Najeriya ku hada kai da addinin ku – Buhari

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari, ya kira ga ‘yan kasa da su sanya bukatar kasa a farko, sannan su rike addini wajen samun hadin kai a tsakani.

A wata sanarwar sakon barka da sallah ga al’ummar musulmi a Najeriya da maitaimaka wa shugaban na musamman kan harkokin yada labaru, Malam Garba Shehu ya fitar, Shugaba Buhari ya ce ‘in har da muna amfani da koyarwar addini, da mun sami mafita kan yawancin matsalolin da muke fuskanta a yanzu.”

A cewar Shugaban ya kamata addini ya zamanto a matsayin abin a za a yi amfani da shi wajen yin abu mai kyau ga kasar nan.

Ya kara da cewa satar kudin kasa da wasu jami’an gwamnati ke yi, wata manuniya ce ta yadda mutane ka barin koyarwar addini.

Shugaban ya kara da cewa ”mutane a yanzu basa soron Allah, inda suke sanya abubuwa su zamanto masu wahala ga wasu”.

Haka kuma ya ce ”shugabanni sukan watsar da shan rantsuwa da suka yi yayin shiga ofis ta hanyar karkatar da kudaden da aka tanada domin walwalar ‘yan kasa zuwa aljihunansu.

A kan matalar tsaro da kuma tsadar rayuwa da kasar ke fuskanta, shugaban ya sha alwashin cewa ba zai gajiya ba har sai ya samar wa ‘yan Najeriya mafita, inda yace yana sane da irin wahalhalun da suke ciki, kuma zai yi maganin hakan nan ba da jimawa ba.

A karshe Shugaban ya taya musulman Najeriya da ma na duniya baki daya murnar bikin sallar layya.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp