fidelitybank

‘Yan Najeriya ku daina yada hotunan jami’an mu da ‘yan ta’adda suka kashe – Sojoji

Date:

Rundunar sojin kasa ta roki jama’a da su daina yada hotunan dakarunta da suka rasa ransu a hare-hare ta shafukan intanet.

Hukumomin sojin suna magana ne kan wani harin kwanton-bauna da wasu ‘yan bindiga suka yi wa sojoji da ke kan hanyarsu ta kai dauki a yayin harin da ‘yan bindiga suka kai kan wasu ma’aikata ‘yan China masu hakar ma’adanai a yankin karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja, ranar Laraba 29 ga watan Yuni, 2022.

Sanarwar da darektan hulda da jama’a na rundunar sojin kasa, Birgediya-Janar Onyema Nwachukwu ya fitar, ta ce, duk da cewa jama’a suna da ‘yancin amfani da kafafen intanet, to amma akwai bukatar su rika hakuri wajen yada hotunan jami’an da aka kashe har sai an sanar da iyalai da ‘yan uwansu.

Haka kuma rundunar ta bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da mara wa jami’nta baya a yakin da suke yi da wadanda ta kira makiyan kasar.

Idan dai ba a manta ba, a lokacin harin ‘yan bindigar sun sace ma’aikata ‘yan kasar China akalla hudu, tare da kashe jami’an tsaro akalla shida wadanda suka kunshi ‘yan sanda da sojoji da kuma ‘yan sintiri na bijilante, kamar yadda ‘yn sanda suka tabbatar wa BBC.

Sai dai kuma wata majiya ta sheda wa BBC, cewa sojoji 4 da ‘yan sandan sintiri (mobile) 4 da kuma ‘yan kungiyar sintiri biyu aka kashe a harin.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp