fidelitybank

‘Yan Najeriya ku daina yada hotunan jami’an mu da ‘yan ta’adda suka kashe – Sojoji

Date:

Rundunar sojin kasa ta roki jama’a da su daina yada hotunan dakarunta da suka rasa ransu a hare-hare ta shafukan intanet.

Hukumomin sojin suna magana ne kan wani harin kwanton-bauna da wasu ‘yan bindiga suka yi wa sojoji da ke kan hanyarsu ta kai dauki a yayin harin da ‘yan bindiga suka kai kan wasu ma’aikata ‘yan China masu hakar ma’adanai a yankin karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja, ranar Laraba 29 ga watan Yuni, 2022.

Sanarwar da darektan hulda da jama’a na rundunar sojin kasa, Birgediya-Janar Onyema Nwachukwu ya fitar, ta ce, duk da cewa jama’a suna da ‘yancin amfani da kafafen intanet, to amma akwai bukatar su rika hakuri wajen yada hotunan jami’an da aka kashe har sai an sanar da iyalai da ‘yan uwansu.

Haka kuma rundunar ta bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da mara wa jami’nta baya a yakin da suke yi da wadanda ta kira makiyan kasar.

Idan dai ba a manta ba, a lokacin harin ‘yan bindigar sun sace ma’aikata ‘yan kasar China akalla hudu, tare da kashe jami’an tsaro akalla shida wadanda suka kunshi ‘yan sanda da sojoji da kuma ‘yan sintiri na bijilante, kamar yadda ‘yn sanda suka tabbatar wa BBC.

Sai dai kuma wata majiya ta sheda wa BBC, cewa sojoji 4 da ‘yan sandan sintiri (mobile) 4 da kuma ‘yan kungiyar sintiri biyu aka kashe a harin.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar Æ´ansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naÉ—a kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka Æ´anbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe Æ´anbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...
X whatsapp