Shugaban kasa Bola Tinubu ya bukaci Musulmi da ‘yan Najeriya baki daya kada su taba yin kasa a gwiwa wajen ganin gwamnatinsa za ta iya juya tattalin arzikin kasar.
Tinubu ya kuma bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da zama ‘yan kasa masu kishin kasa saboda yadda ake aiwatar da manufofin samar da ci gaba ga kowa da kowa.
Ya bayar da wannan tabbacin ne a ranar Laraba a Legas, lokacin da ya bi sahun musulmin da suka gudanar da sallar Eid-el-Fitr.
Da yake jawabi ga manema labarai bayan kammala Sallar Idi a filin Idi da ke barikin Dodan, Shugaban kasar ya ce ana kan aiwatar da ajandar sabunta fata na gwamnatinsa da ke da nufin kawo ci gaba ga ‘yan Najeriya.
“Ci gaba da imani da gwamnatita kuma ku kasance masu kishin kasa.”
Da yake kwadaitar da al’ummar musulmin da suke murnar kammala azumin watan Ramadan, domin mika darajar sadaukarwa da juriya fiye da lokacin azumi, Tinubu ya jaddada bukatar ‘yan Nijeriya su ba da fifiko wajen baje kolin soyayya ga kasarsu.
“Ya kamata a kiyaye juriya da sadaukarwa da muka nuna kuma muka yi a cikin wadannan watanni. Ka zama mai bayarwa na alheri da fara’a. Dole ne mu ƙaunaci ƙasarmu fiye da kowace ƙasa, domin ita ce kaɗai muke da ita.
“Dole ne mu ci gaba da kare mutuncin gwamnatinmu da shugabancinmu.
“Ajandar sabunta bege na nan da rai, lafiya kuma lau, kuma ya kamata ‘yan Nijeriya su ci gaba da kasancewa da bege. Idan babu bege, babu ceto. Idan babu fata, babu wani ci gaba. Idan babu bege, babu rayuwa. Eid Mubarak,’’ Shugaban ya shaida wa manema labarai a karshen addu’ar da babban limamin jihar Legas, Sheikh Sulaiman Oluwatoyin Abou-Nolla ya jagoranta.
Tun da farko a hudubar tasa, babban limamin ya bukaci ‘yan Najeriya da su guji duk wani abu na tashin hankali, tabbatar da zaman lafiya da kuma ci gaba da imani a kasar.
Ya kuma bukaci masu rike da madafun iko da su ci gaba da yin amanna da rantsuwar da aka yi musu, su kuma yi kokarin ganin an rage wa masu karamin karfi radadin talauci.
“Kada mu manta da ’yan uwanmu a Gaza da sauran wuraren da ake rikici,” in ji Babban Limamin.
Ya kuma yi addu’ar Allah ya yi masa jagora, da hikima, da kuma kariya ga shugaban kasa da gwamnatin jihar Legas, da kuma zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar nan.