fidelitybank

‘Yan Najeriya ba za ku yi da na sani ba a kai na – Tinubu

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Sanata Bola Ahmed Tinubu, ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa, ba za su yi nadamar zaban shi a kan karagar mulki a zaben 2023 ba.

Da yake jawabi a Kaduna ranar Talata a taron shiyyar Arewa maso Yamma, dan takarar shugaban kasar ya ce, “Ina so in tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa zabe na a matsayin shugaban kasar nan zai zama tirjiya ga dukkan kalubalen da ‘yan kasar ke fuskanta. ”

Ya kuma gargadi duk masu tayar da zaune tsaye da su nemo hanyoyin da za su bi, yana mai tabbatar da cewa duk wanda bai yarda da zaman lafiya da hadin kai da ci gaban kasa ba, ba zai samu sauki ba idan a karshe ya zama shugaban kasar.

Ya kara da cewa kalubalen tsaro da ake fuskanta yanzu zai zama tarihi kuma ‘yan Najeriya na iya gudanar da harkokinsu na yau da kullun.

Ya bayyana cewa, “Gwamnatina za ta yi duk mai yiwuwa wajen samar da ayyukan yi, ta yadda matasanmu za su fahimci halin da suke ciki. Za a ba da duk wata dama ta baiwa manoman mu yanayin da za su iya komawa gona da abubuwan da suka dace don bunkasa noma a kowane bangare na kasar nan”.

Ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su shirya musu katin zabe, yana mai cewa su shirya zaben ‘yan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben badi.

Tun da farko Gwamna Nasir El-Rufai ya godewa al’ummar yankin Arewa maso Yamma da suka zo Kaduna domin gudanar da gangamin, ya kuma umarce su da su tabbatar sun zabi jam’iyyar APC a dukkan matakai a zaben badi.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp