fidelitybank

‘Yan Najeriya ba cimma zaune ba ne a mulki na – Tinubu

Date:

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya jaddada aniyarsa ta gyara Najeriya, yana mai bayyana ƴan ƙasa da cewa masu ƙwazo ne, saboda haka babu wani dalili da zai sanya su zauna cikin talauci.

Tinubu ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi baƙuncin tawagar wasu dattawan ƙasar, da suka haɗar da jagororin jam’iyyun APC da PDP, a fadar shugaban ƙasa.

“Mu ba ci-ma-zaune ba ne, muna da arziƙi. Abin da muke buƙata shi ne taimakon junanmu, mu zama ‘yan uwa nagari. Ni ba shugaban ƙasar da zai ba da uzurririka,” kamar yadda mai magana da yawunsa ya bayyana.

“Zan yi aiki tuƙuru da manufofi masu kyau, da sadaukarwa da ƙwarin gwiwa don samar da arziƙi ga ƴan Najeriya,babu wani dalili da zai sanya mu zauna cikin talauci, ba za mu ci baya ba,”

Shugaban Tinubu ya ƙara da cewa “Ba wani abu ba ne, yanzu muna fuskantar tsanani, amma daɗin na gaba. Za mu cimma muradunmu tare da cika burukan kakanninmu. Ina samun ƙwarin gwiwa daga ƴan ƙasar da nake mulki.”

Tawagar shugabannin sun ce sun yi amanar cewa zai ciyar da Najeriya gaba, zai kuma cika alƙawurran da yayi wa ƴan ƙasar.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp