Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa kimanin ‘yan Najeriya 2,090 ne za su dawo gida Najeriya daga kasar Ukraine a ranar Alhamis, bayan farmakin da sojojin kasar Rasha suka kai a Ukraine.
Jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa, wadannan ‘yan Najeriya da suka makale sun nuna sha’awar komawa gida, bayan sun tsere zuwa kasashen Hungary, Poland, Romania, da Slovakia.
Da yake zantawa da manema labarai a ranar Laraba a Abuja, babban sakataren ma’aikatar harkokin wajen kasar, Gabriel Aduda, ya bayyana cewa, jiragen da aka yi hayar za su tashi ne a ranar Laraba 2 ga Maris, 2022, domin dauko ‘yan Najeriya da aka kwashe zuwa gida.
Ya ce: “Aiki da hanyar da kamfanonin jiragen suka yi sune kamar haka: Max Air zuwa Romania mutum 560, Air Peace zuwa Poland mutane 364 da Air Peace zuwa Hungary 360.
Aduda ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatin tarayya na aiki ba dare ba rana domin dawo da ‘yan Najeriya gida lafiya.