fidelitybank

‘Yan majalisun da suka bar ofishin su sun wawure komai gatta Talabijin ba su bari ba – Oshiomhole

Date:

Tsohon Gwamnan Jihar Edo kuma Sanata mai wakiltar Edo ta Arewa, Adams Oshiomhole, ya bayyana kaduwarsa kan abin da ya kira matakin barnatar da kadarorin Majalisar Dokoki ta kasa da ‘yan majalisar suka yi.

Oshiomhole ya bayyana cewa, duk da kasancewar jami’an tsaro maza da mata, sai da wasu Sanatoci da ‘yan majalisar wakilai na baya-bayan nan suka wawure talbijin, katifu da kujeru.

Oshiomhole ya bayyana hakan ne a lokacin da ya bayyana a gidan talabijin na Channels Television na Sunday Politics.

A cewarsa, tsoffin ‘yan majalisar sun bar ofisoshinsu ne a ruguje da ramuka a bango, inda suka ce sai da ya biya ya gyara ofishinsa kafin amfani da shi.

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, ya jaddada cewa an kuma barnata a ofisoshin da wasu manyan jami’an majalisar da suka bari, wadanda ya ki bayyana sunayensu.

“Bari in fada muku abu daya da majalisar kasa ba ta magana a kai kuma ban san dalilin da ya sa wadanda ke da hakkin yin magana ba sa magana a kai.

“Na yi matukar kaduwa da matakin barnatar da kadarorin Majalisar Tarayya. An kwashe gidajen Talabijin, an kwashe katifu, an kwashe kujerun Sanatoci. Sai da na yi amfani da kudina, wani kuma ya yanke shawarar kawo mani na’urar bugawa, don ba ni kwamfutar da zan yi amfani da ita a ofishina. Sai da na sayi kafet na biya kudin gyara shi. Dole ne in biya wasu matasa don tsaftace ofishin don mayar da sabon kafet. Sai da na biya na gyara ofishina. Zan kawo muku rasit.

“Ba zan iya fahimtar dalilin da ya sa da kuma yadda majalisar dattawan da ta zauna a ranar Lahadi kafin a kaddamar da mu a ranar Talata mai zuwa, kuma matakin barna ya faru, kuma muna da daruruwan jami’an tsaro maza da mata a majalisar dokokin kasar. Ba zan iya fahimtar abin da ya faru ba. Kuna samun ramuka a bango, har ma a ofisoshin manyan hafsoshin majalisar dattawa, wadanda ba zan iya ambata ba.

“Mutane sun gaya min cewa akwai irin wannan barna a majalisar wakilai,” in ji Oshiomhole.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp