‘Yan majalisar dokokin jihar Enugu shida sun sauya sheƙa daga jam’iyyar LP zuwa PDP, shekara guda bayan zaɓe.
Kakakin majalisar jihar Chief Uche Ugwu ne ya sanar da ficewar tasu a wata wasika da ya karanta yayin wani zama da aka yi a ranar Alhamis
Waɗanda suka sauya sheƙar sun haɗa da shugaban masu rinjaye Mr Johnson Ani daga Enugu ta arewa, da mai tsawatarwar majalisar Mr Ejike Eze da ke wakiltar Igbo-Eze, sai mataimakiyar mai tsawatarwar Ms Princess Ugwu daga Enugu ta Kudu.
Sauran sun haɗa da Mr Pius Ezugwu da da Mista Williams Amuka da kuma Mista Osita Eze.
Wasikar ta ce mutanen sun sauya sheƙar ne dalilin rikice-rikice da rabuwar kai da suka ƙi-ci suka ƙi-cinyewa a matakin jam’iyyar na ƙasa da sauran rassanta na jihohi.
Sun ce wannan rikici da har ya kai wasu ga ɗaukar mataki na shari’a babu abin da za su haifar sai koma baya ga jam’iyyar. Waɗanda aka zaɓa kuma ba za su iya yin abin da mutane suka zaɓe su domin shi ba.