Jam’iyyar Peoples Democratic Party, PDP Majalisar Dattawa a ranar Alhamis ta tashi don warware rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar.
Wannan ci gaban ya biyo bayan wata ganawar sirri ta sama da sa’o’i uku wanda shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Sanata Abba Moro ya jagoranta.
Da yake zantawa da manema labarai bayan taron, Moro wanda ke wakiltar mazabar Benuwe ta Kudu ya bayyana cewa an ba da umarnin fadada kwamitin da ya hada da tsaffin gwamnonin jam’iyyar PDP da wasu fitattun shugabanni su yi mu’amala da ’ya’yan da suka ji haushi.
Ya ce, ‘yan kwamitin, an dora musu alhakin gano wuraren da ake korafe-korafe da kuma tabbatar da an warware su cikin lumana kafin su mika rahotonsu domin jam’iyyar ta ci gaba.