fidelitybank

‘Yan majalisar Amurka sun bukaci Najeriya ta saki jami’in Binance

Date:

Wasu ‘yan majalisar dokokin Amurka, sun buƙaci gwamnatin Najeriya ta saki babban jami’in kamfanin hada-hadar kudin intanet na Binance, Tigran Gambaryan da hukumomi sukae tsare shi a gidan yari na Kuje da ke Abuja, bayan da suka ziyarci jami’in a ranar Laraba.

A wani hoton bidiyo da ya sanya a shafinsa na X, ɗan majalisar wakilai French Hill tare da takwararsa Chrissy Houlahan, ya ce a lokacin da suka ziyarci Gambaryan, wanda ɗan Amurka ne, sun ga cewa yana fama da wasu matsaloli na rashin kyawun gidan ajiya da gyaran halin.

Ƴan majalisar dokokin na Amurka, sun yi zargin cewa an hana Gambaryan samun kulawar da ta dace ga lafiyarsa, inda ya kamu da cutar zazzaɓin cizon sauro da kuma ta sanyin haƙarƙari wato (nimoniya).

Sun kuma buƙaci ofishin jakadancin Amurka da ke kasar nan da ya nemi a saki jami’in bisa dalilai na jinƙai da rashin laifi, saboda mummunan halin da gidan yarin yake ciki.

A watan Fabarairu ne aka kama Tigran Gambaryan tare da abokin aikinsa Nadeem Anjarwalla, mai takardar shedar ɗan ƙasar Birtaniya da Kenya.

Sai dai takwaran nasa Nadeem Anjarwalla ya tsere daga hannun hukomomin tsaro.

Wannan kiran ya biyo bayan buƙatar da wasu yan majalisar dokokin na Amurka su 18 ne suka gabatar ga Shugaban Amurka Joe Biden domin ya sa baki a saki Mista Gambaryan.

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp