A yau Talata ne ake sa ran majalisar wakilai za ta koma zama a zauren majalisar, bayan hutun da da ta tafi a watan da ya gabata.
Bayan zaman ta na farko na shekarar 2025 a ranar 14 ga watan Janairu, majalisar ta ɗage zama zuwa 28 ga watan domin bai wa kwamitoci damar kammala ayyukansu kan dokar kasafin kuɗi da shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya gabatar a gaban Majalisar.
Ana sa ran cewa a zaman na yau batun dokar haraji nan mai sarƙaƙiya na daga cikin batutuwan da ƴan majalisar za su mayar da hankali kai.
Ƙudurin harajin, wanda shugaba Tinubu ya gabatar wa Majalisar a shekarar da ta gabata ya janyo zazzafar muhawar a faɗin ƙasar.
Lamarin da ya sanya aka jingine yanke hukunci a kansa.
Daga baya gwamnonin jihohin ƙasar sun yi wa ƙudurin gyaran fuska, kuma da alama shugaban ƙasar ya yi maraba da hakan, inda ya yaba wa gwamnonin sannan ya buƙaci majalisar dokokin ta hanzarta amincewa da dokar.