fidelitybank

‘Yan majalissa sun umarci jami’an tsaro su tare hanyoyin da ‘yan ta’adda ke tserewa

Date:

‘Yan majalisar dattawa sun umarci sojoji da sauran jami’an tsaron kasar da su sanya ido sosai tare da tare duk wasu hanyoyin da ‘yan ta’adda da barayin daji ke bi suna tserewa.

Jaridar DailyTrust ta rawaito cewa, ‘yan majalisar sun bayar da umarnin ne bayan gabatar da kuduri da mataimakin Gagarabadau, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi na jihar Neja ya yi, sakamakon sabbin hare-hare da satar mutane da ake yi a yankunan kananan hukumomin Mariga da Mashegu da Kontagora da kuma Borgu na jihar Neja.

Sanatan ya ce, “Sakamakon muggan hare-haren da sojoji da sauran jami’an tsaro ke kai wa ‘yan ta’adda da barayin daji da suka addabi yankunan gabashin jihar Sokoto da Zamfara, ‘yan ta’adda na ta tserewa suna shiga jihar Neja, ya kamata a tsara hare-haren da ake kai wa ‘yan ta’addar da kyau yadda ya kamata, ta yadda za a datse duk wata hanya da suke bi suna guduwa suna shiga sassan jihar Neja”.

Majalisar ta umarci hukumar bayar da agajin gaggawa NEMA da ta samar da kayan abinci da sauran muhimman abubuwa more rayuwa ga mutanen kauyukan da hare-haren ‘yan ta’addar ke shafa da kuma ‘yan gudun hijira a yankunan kananan hukumomin Mariga da Mashegu da Kontagora da kuma Borgu.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuÉ—in gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuÉ—in gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuÉ—a

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiÉ—a wa Isra'ila wasu...
X whatsapp