‘Yan majalisar dattawa sun umarci sojoji da sauran jami’an tsaron kasar da su sanya ido sosai tare da tare duk wasu hanyoyin da ‘yan ta’adda da barayin daji ke bi suna tserewa.
Jaridar DailyTrust ta rawaito cewa, ‘yan majalisar sun bayar da umarnin ne bayan gabatar da kuduri da mataimakin Gagarabadau, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi na jihar Neja ya yi, sakamakon sabbin hare-hare da satar mutane da ake yi a yankunan kananan hukumomin Mariga da Mashegu da Kontagora da kuma Borgu na jihar Neja.
Sanatan ya ce, “Sakamakon muggan hare-haren da sojoji da sauran jami’an tsaro ke kai wa ‘yan ta’adda da barayin daji da suka addabi yankunan gabashin jihar Sokoto da Zamfara, ‘yan ta’adda na ta tserewa suna shiga jihar Neja, ya kamata a tsara hare-haren da ake kai wa ‘yan ta’addar da kyau yadda ya kamata, ta yadda za a datse duk wata hanya da suke bi suna guduwa suna shiga sassan jihar Neja”.
Majalisar ta umarci hukumar bayar da agajin gaggawa NEMA da ta samar da kayan abinci da sauran muhimman abubuwa more rayuwa ga mutanen kauyukan da hare-haren ‘yan ta’addar ke shafa da kuma ‘yan gudun hijira a yankunan kananan hukumomin Mariga da Mashegu da Kontagora da kuma Borgu.