fidelitybank

‘Yan majalisa sun fara shirin tsige mataimakin gwamnan Edo

Date:

‘Yan majalisar dokokin jihar Edo sun fara shirin tsige mataimakin gwamnan jihar, Philip Shaibu.

An karanta koken tsige mataimakin gwamnan ne a ranar Laraba a zaman majalisar.

Shugabar masu rinjaye, Charity Aiguobarueghian, wacce ta karanta karar tsige mataimakin gwamnan a zauren majalisar, ta ce mambobin 21 cikin 24 ne suka sanya hannu kan karar da suka shigar a kan mataimakin gwamnan.

Aiguobarueghian, ya ce an gabatar da karar ne a ranar 5 ga Maris, 2024, ya ce adadin mambobin da suka rattaba hannu kan takardar ya zarce kashi biyu bisa uku da ya tanada a sashe na 188 (2a) na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya.

Ya ce an mika koken ne ga kakakin majalisar, Blessing Agbebaku.

Shugaban majalisar wanda ya amince da karbar koken ya ce an gabatar da karar ne bisa wasu dalilai guda biyu wadanda ba a bayyana su ba.

Sai dai majalisar ta baiwa mataimakin gwamnan wa’adin kwanaki bakwai ya amsa bukatar.

Shugaban majalisar ya umurci magatakardar majalisar, Yahaya Omogbai, da ya ba da sanarwar tsige Shaibu.

Watakila sanarwar tsige Shaibu ba ta rasa nasaba da rikicin sa da gwamnan jihar Godwin Obaseki wanda ya kai shi ga rashin nasara a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP da aka kammala a jihar.

Idan dai za a iya tunawa, Shaibu ya yi zargin yunkurin tsige shi daga mukaminsa, yana mai cewa burinsa na zama gwamna ne ke da alhakin shirin.

An zabe shi a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP a daidai lokacin zaben fidda gwani da aka gudanar a gidansa da ke birnin Benin, babban birnin jihar.

An kuma bayyana Asue Ighodalo a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP da ya gudana a filin wasa na Samuel Ogbemudia da ke Benin.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp