Shugaban ɗaya ɓangaren majalisar dokokin Rivers, Edison Ehie ya ayyana kujerun ƴan majalisa 27 da a baya-bayan nan suka fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC a matsayin na waɗanda babu kowa a kai.
An ɗauki wannan matakin ne da safiyar yau Laraba yayin zaman majalisar da Ehie ya jagoranta inda hakan ya zo daidai lokacin da ake rushe ginin majalisar dokokin.
Lamarin ya faru ne sakamakon sauya sheƙar da mambobin 27 suka yi ƙarƙashin jagorancin Martin Amaewhule, wanda shi ne shugaban ɗaya ɓangaren majalisar da ke goyon bayan tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike.
Majalisar dokokin jihar mai mambobi 32 ta tsunduma cikin rikicin shugabanci tun watan Oktoba inda ɓangarorin biyu da ke rikici da juna ke fafutukar ƙwace ikon majalisar.
Wata babbar kotu a Patakwal a baya-bayan nan kuma ta tabbatar da Ehie a matsayin halastaccen shugaban majalisar.
Kotun ta kuma hana magoya bayan Wike daga shiga harabar majalisar har sai an gama gyara majalisar da gwamnatin jihar ta ba da umarni.