Hukumar bayar da agajin gaggawa ta NEMA a hukumance ta tabbatar da cewa, fashewar da ta afku a Abuja da yammacin ranar litinin ta faru ne sakamakon wani harin kunar bakin wake.
NEMA, a wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a lokacin da wani sanye da bama-bamai ya yi yunkurin kutsawa cikin Rundunar Sojin Mogadishu da ke kan hanyar Mararaba zuwa Nyanya.
Rahotanni sun bayyana cewa na’urar ta tashi ne a lokacin yunkurin, inda nan take ta kashe dan kunar bakin waken tare da jikkata wani mai wucewa.
Mutumin da ya ji rauni, farar hula ne, nan take sashen kakkabe bama-bamai na rundunar ‘yan sandan Najeriya ya dauke shi zuwa Asibitin kasa domin yi masa magani.
Fashewar wadda ta afku da misalin karfe 1:47 na daren ranar Litinin, ya sa hukumomi da dama suka mayar da martani cikin gaggawa, da suka hada da NEMA, Sojoji, Rundunar ‘yan sandan Najeriya, DSS, da kuma hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC).
Idan dai za a iya tunawa, rundunar sojin Najeriya da rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, sun tabbatar da faruwar fashewar lamarin, tare da bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da bincike.
“Bayanin farko sun nuna cewa dan kunar bakin waken na kokarin shiga bariki ba tare da izini ba lokacin da bam din ya tashi.
” Kwararru a fannin shari’a sun fara bincike kan lamarin, kuma an kammala aikin da karfe 5:29 na yamma.” NEMA ta bayyana.