fidelitybank

‘Yan kunar bakin wake sun nemi Sojoji ne kai tsaye – NEMA

Date:

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta NEMA a hukumance ta tabbatar da cewa, fashewar da ta afku a Abuja da yammacin ranar litinin ta faru ne sakamakon wani harin kunar bakin wake.

NEMA, a wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a lokacin da wani sanye da bama-bamai ya yi yunkurin kutsawa cikin Rundunar Sojin Mogadishu da ke kan hanyar Mararaba zuwa Nyanya.

Rahotanni sun bayyana cewa na’urar ta tashi ne a lokacin yunkurin, inda nan take ta kashe dan kunar bakin waken tare da jikkata wani mai wucewa.

Mutumin da ya ji rauni, farar hula ne, nan take sashen kakkabe bama-bamai na rundunar ‘yan sandan Najeriya ya dauke shi zuwa Asibitin kasa domin yi masa magani.

Fashewar wadda ta afku da misalin karfe 1:47 na daren ranar Litinin, ya sa hukumomi da dama suka mayar da martani cikin gaggawa, da suka hada da NEMA, Sojoji, Rundunar ‘yan sandan Najeriya, DSS, da kuma hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC).

Idan dai za a iya tunawa, rundunar sojin Najeriya da rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, sun tabbatar da faruwar fashewar lamarin, tare da bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da bincike.

“Bayanin farko sun nuna cewa dan kunar bakin waken na kokarin shiga bariki ba tare da izini ba lokacin da bam din ya tashi.

” Kwararru a fannin shari’a sun fara bincike kan lamarin, kuma an kammala aikin da karfe 5:29 na yamma.” NEMA ta bayyana.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp