fidelitybank

‘Yan kunar bakin wake sun nemi Sojoji ne kai tsaye – NEMA

Date:

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta NEMA a hukumance ta tabbatar da cewa, fashewar da ta afku a Abuja da yammacin ranar litinin ta faru ne sakamakon wani harin kunar bakin wake.

NEMA, a wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a lokacin da wani sanye da bama-bamai ya yi yunkurin kutsawa cikin Rundunar Sojin Mogadishu da ke kan hanyar Mararaba zuwa Nyanya.

Rahotanni sun bayyana cewa na’urar ta tashi ne a lokacin yunkurin, inda nan take ta kashe dan kunar bakin waken tare da jikkata wani mai wucewa.

Mutumin da ya ji rauni, farar hula ne, nan take sashen kakkabe bama-bamai na rundunar ‘yan sandan Najeriya ya dauke shi zuwa Asibitin kasa domin yi masa magani.

Fashewar wadda ta afku da misalin karfe 1:47 na daren ranar Litinin, ya sa hukumomi da dama suka mayar da martani cikin gaggawa, da suka hada da NEMA, Sojoji, Rundunar ‘yan sandan Najeriya, DSS, da kuma hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC).

Idan dai za a iya tunawa, rundunar sojin Najeriya da rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, sun tabbatar da faruwar fashewar lamarin, tare da bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da bincike.

“Bayanin farko sun nuna cewa dan kunar bakin waken na kokarin shiga bariki ba tare da izini ba lokacin da bam din ya tashi.

” Kwararru a fannin shari’a sun fara bincike kan lamarin, kuma an kammala aikin da karfe 5:29 na yamma.” NEMA ta bayyana.

uanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaÉ—an wajen tsaron Æ™asa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haÉ—in...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...
X whatsapp