fidelitybank

‘Yan kunar bakin wake sun nemi Sojoji ne kai tsaye – NEMA

Date:

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta NEMA a hukumance ta tabbatar da cewa, fashewar da ta afku a Abuja da yammacin ranar litinin ta faru ne sakamakon wani harin kunar bakin wake.

NEMA, a wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a lokacin da wani sanye da bama-bamai ya yi yunkurin kutsawa cikin Rundunar Sojin Mogadishu da ke kan hanyar Mararaba zuwa Nyanya.

Rahotanni sun bayyana cewa na’urar ta tashi ne a lokacin yunkurin, inda nan take ta kashe dan kunar bakin waken tare da jikkata wani mai wucewa.

Mutumin da ya ji rauni, farar hula ne, nan take sashen kakkabe bama-bamai na rundunar ‘yan sandan Najeriya ya dauke shi zuwa Asibitin kasa domin yi masa magani.

Fashewar wadda ta afku da misalin karfe 1:47 na daren ranar Litinin, ya sa hukumomi da dama suka mayar da martani cikin gaggawa, da suka hada da NEMA, Sojoji, Rundunar ‘yan sandan Najeriya, DSS, da kuma hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC).

Idan dai za a iya tunawa, rundunar sojin Najeriya da rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, sun tabbatar da faruwar fashewar lamarin, tare da bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da bincike.

“Bayanin farko sun nuna cewa dan kunar bakin waken na kokarin shiga bariki ba tare da izini ba lokacin da bam din ya tashi.

” Kwararru a fannin shari’a sun fara bincike kan lamarin, kuma an kammala aikin da karfe 5:29 na yamma.” NEMA ta bayyana.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haÉ—aka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...
X whatsapp