fidelitybank

‘Yan kasuwar Kantin Kwari sun yi sallar samun saukin tsadar rayuwa a Najeriya

Date:

Wasu ƴan kasuwa da ke hada-hada a kasuwar Kantin kwari da ke birnin Kano sun gudanar da addu’o’in neman samun sauƙi kan matsin tattalin arziƙi da ake ciki a Najeriya.

Ƴan kasuwar sun fito daga kantunansu inda suka gudanar da sallah da addu’o’i tare da neman ɗauki daga ubangiji.

Ɗaya daga cikin ƴan kasuwar mai suna Hamisu Sani ya shaida wa BBC cewa al’amura sun rincaɓe inda yanzu haka abinci ke gagarar al’umma.

Ya ce “mun gudanar da addu’o’i domin samun ɗauki daga ubangiji kan wannan hali, domin ba mu san abin da shugabanni ke yi kan wannan hali ba.”

Ya ƙara da cewa “Buhun shinkafa da na sukari a yanzu haka sun gagari talaka.”

Tashin kayan masarufi ya munana a Najeriya cikin kwanakin nan.

Lamarin ya ƙazance ne sanadiyyar wasu daga cikin shirye-shiryen da gwamnati ta ɓullo da su, kamar na cire tallafin man fetur.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp