Zanga-zangar ta barke a garuruwa da biranen kasar Kazakhstan da dama, tun bayan da gwamnatin kasar ta tsakiyar yankin Asiya ta dage farashin man iskar gas da kuma tsadar man fetur da ya tashi a kasar.
Zanga-zangar dai ta shafi dubban mutane, wanda su ka fara ne tun a ranar 2 ga watan Janairu, kwana guda bayan da aka daga farashin Gas a garin Zhanaozen, wurin da aka yi kazamin fada tsakanin masu zanga-zanga da ‘yan sanda tun bayan samun ‘yancin kai daga Tarayyar Soviet.
Masu zanga-zangar a Zhanaozen, cibiyar masana’antar mai da ke yammacin lardin Mangistau inda a ka kashe mutane da dama a zanga-zangar da a ka yi a shekara ta 2011, bayan korar ma’aikatan mai, wanda suka bukaci a rage farashin Gas daga kudin sun a tenge 120 ($ 0.27) a kowace lita zuwa matakin da ya dace.
Dillalai sun amince su rage farashin, amma gwamnatin shugaban kasar karkashin, Kassym-Jomart Tokayev, ta ce kara rage farashin ba zai yiwu ba, saboda tsadar kayayyakin da a ke kashewa.