fidelitybank

‘Yan Kannywood na jimamin mutuwar Kafi Gwamna na Kwana Casa’in

Date:

‘Yan fim da furodusoshi da daraktoci da masu ruwa da tsaki a masana’antar Kannywood sun yi ta bayyana jimami da alhinin rasuwar fitaccen dan wasan nan Umar Yahaya Malumfashi da aka fi sani da Bankaura ko Ka fi Gwamna.

A daren Talata 27 ga watan Satumba ne, Allah ya yi wa fitaccen jarumin rasuwa a wani asibiti da birnin Kano a arewacin Najeriya, bayan fama da rashin lafiya.

Umar Malumfashi da aka fi sani da sunan Bankaura a cikin tsofaffin finan-finan Hausa tun kafin kafa masana’antar Kannywood, yayin da a wannan zamanin kuma ake kiransa da sunan Yakubu ka fi gwamna, saboda rawar da ya ke takawa a shirin Arewa24 mai dogon zango wato Kwana Casa’in.

Bankaura ya taka muhimmiyar rawa domin ciyar da masana’antar Kannywood gaba, yana daya daga cikin ‘yan wasan da suka dade a wannan fagge.

Ya yi zamani da manyan iyaye mata da maza a masana’antar, irin su marigayiya Hajiya Amina Garba (Hajiya Dumba, ko Hajiyar falo), da marigayiya Hawwa Ali Dodo (Biba) da marigayiya Jamila Haruna, da su Hajara Usman, Saratu Gidado (daso) da sauran su.

An yi amanna da cewa yana daya daga cikin wadanda ke tafiya da zamani a masana’antar Kannywood, karamin misali shi ne rawar da ya taka a shiri mai dogon zango na Kwana Casa’in.

Tuni abokan sana’arsa da makusanta suka bazama shafukan sada zumunta domin bayyana alhini da ta’aziyyar rasuwarsa.

Alhaji Ado Gidan Dabino na daya daga cikinsu, musamman ganin ya na daya daga cikin wadanda sukai wa marigayin gani na karshe.

Gidan Dabino ya wallafa hotonsa tare da marigayin, a wurin daukar shirin Kwana Casa’in suna duba wasu takardu, ya wallafa.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp