fidelitybank

‘Yan Kannywood na jimamin mutuwar Kafi Gwamna na Kwana Casa’in

Date:

‘Yan fim da furodusoshi da daraktoci da masu ruwa da tsaki a masana’antar Kannywood sun yi ta bayyana jimami da alhinin rasuwar fitaccen dan wasan nan Umar Yahaya Malumfashi da aka fi sani da Bankaura ko Ka fi Gwamna.

A daren Talata 27 ga watan Satumba ne, Allah ya yi wa fitaccen jarumin rasuwa a wani asibiti da birnin Kano a arewacin Najeriya, bayan fama da rashin lafiya.

Umar Malumfashi da aka fi sani da sunan Bankaura a cikin tsofaffin finan-finan Hausa tun kafin kafa masana’antar Kannywood, yayin da a wannan zamanin kuma ake kiransa da sunan Yakubu ka fi gwamna, saboda rawar da ya ke takawa a shirin Arewa24 mai dogon zango wato Kwana Casa’in.

Bankaura ya taka muhimmiyar rawa domin ciyar da masana’antar Kannywood gaba, yana daya daga cikin ‘yan wasan da suka dade a wannan fagge.

Ya yi zamani da manyan iyaye mata da maza a masana’antar, irin su marigayiya Hajiya Amina Garba (Hajiya Dumba, ko Hajiyar falo), da marigayiya Hawwa Ali Dodo (Biba) da marigayiya Jamila Haruna, da su Hajara Usman, Saratu Gidado (daso) da sauran su.

An yi amanna da cewa yana daya daga cikin wadanda ke tafiya da zamani a masana’antar Kannywood, karamin misali shi ne rawar da ya taka a shiri mai dogon zango na Kwana Casa’in.

Tuni abokan sana’arsa da makusanta suka bazama shafukan sada zumunta domin bayyana alhini da ta’aziyyar rasuwarsa.

Alhaji Ado Gidan Dabino na daya daga cikinsu, musamman ganin ya na daya daga cikin wadanda sukai wa marigayin gani na karshe.

Gidan Dabino ya wallafa hotonsa tare da marigayin, a wurin daukar shirin Kwana Casa’in suna duba wasu takardu, ya wallafa.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp