fidelitybank

‘Yan Jigawa ku yi wa Tinubu rubdugun kuri’u a 2023 – Badaru

Date:

Gwamna Muhammad Badaru na jihar Jigawa, a ranar Laraba ya bukaci al’ummar jihar da su zabi Sen. Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a 2023 domin ci gaba.

Gwamnan ya ce zaben Tinubu na da matukar muhimmanci domin ganin ya ci gaba da ayyukan titin, layin dogo da sauran ayyukan gwamnatin tarayya da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a jihar.

Badaru yayi magana ne a Gumel jim kadan bayan gabatar da tutoci ga ’yan takarar jam’iyyar APC da ke neman mukamai daban-daban a yankin Sanatan Jigawa ta Arewa maso Yamma.

Ya ce APC ce kadai jam’iyyar da jama’a suka amince da ita a jihar da ma Najeriya baki daya.

“Mun cika kusan dukkan alkawuran da muka dauka a yakin neman zabe, domin babu wata al’umma da har yanzu ba ta ci gajiyar ayyuka daya ko sama da haka ba da babbar jam’iyyar mu ta APC.

“Muna da gado a jihar kuma ina tabbatar muku da cewa zaben jam’iyyar APC a dukkan matakai zai tabbatar da ci gaba da gudanar da irin wadannan ayyuka da shirye-shirye,” in ji gwamnan yana cewa.

Badaru ya bukaci jama’a da su kada kuri’a ga dan takarar gwamna na jam’iyyar a jihar, Malam Umar Namadi.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp