fidelitybank

‘Yan Jarida ne madogarar al’umma – Ejiro Umukoro

Date:

An dora wa ‘yan jarida alhakin aikin zurfafa bincike kan rahotannin da za su yi tasiri ga ci gaban al’umma da hanyoyin magance matsaloli.

Wannan wani bangare ne na tattaunawa a wani taron karawa juna sani na Mastermind Media Pro wanda ‘yar jarida da ta samu lambar yabo da yawa kuma marubuciyar littafin Distortion, Lady Ejiro Umukoro ta shirya, wadda LightRay Media ta hada a cibiyar Aquire da ke Effurun, yankin karamar hukumar Uvwie ta jihar Delta ranar Litinin.

Wasu batutuwan da aka tattauna a wajen taron sun hada da gano gibin da ke tattare da kafafen yada labarai, dalilin da ya sa suke da su, da abin da za a iya yi, domin magance su da kuma hanyoyin da kwararru za su hada kai, domin bunkasa sana’ar da kuma tabbatar da martabarta aikin.

Yayin taron an kuma yi musayar ra’ayi tsakanin ‘yan jarida kusan 20 da aka zabo daga yankunan Warri, Sapele da Ughelli na jihar.

Sun bayyana rashin tsaro, rashin isassun horo, rashin sabunta kima da walwala, da kuma rashin mutuntawa da kuma tsoratar da ma’aikata, a matsayin kalubalen aikin jarida a Najeriya.

Da take magana kan matakan da ‘yan jarida za su bi wajen cike gibin, wata ‘yar jarida mai suna Omamuzo Efidhere, ta bayyana ra’ayin ta na cewa, abokan aikin za su iya hada kai, domin samar da tambayoyin, idan daya daga cikinsu ya samu damar yin hira da wani fitaccen mutumi.

Ta ce, “Ta haka, za a iya magance batutuwan da suka fi yawa, kuma watakila, domin ci gaban al’umma.”

Wasu kuma sun ba da shawarar hadin gwiwa tsakanin abokan aiki, musamman wajen raba rahotanni, gaskiya da ‘yan uwantaka.

Wadanda suka shirya taron na LightRay Media sun bayyana cewa, wani shiri ne na mayar da hankali wajen tunawa da gudumawar mai koyarwa da jagoranci a fannin yada labarai da aikin jarida.

Ejiro Umukoro ya bukaci ‘yan jarida a fadin jihar Delta da su bibiyi hanyoyin warwarewa ga aikin jarida na ci gaba, domin su yi wa kansu wata kafa a harkar yada labarai.

Ta kuma karfafa gwiwar manema labarai da su fahimci damar da za su horar da su da kuma bunkasa kansu domin bunkasa kwarewarsu wajen bayar da rahoto

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp