Tsohon dan majalisar dokoki kuma mai sharhi kan zamantakewar al’umma, Shehu Sani, ya bukaci mazauna yankin Kudu maso Gabas da su bijirewa umarnin zaman gida da bangaren Simon Ekpa na kungiyar ‘yan asalin yankin Biyafara, IPOB su kasance masu neman zaman lafiya.
Sanarwan Sanata Sani na kunshe ne a wani sako da ya wallafa a shafin sa na Twitter ranar Alhamis.
Idan dai za a iya tunawa, kungiyar ‘yan awaren da ta balle ta yi barazanar bayar da dokar zaman gida a yankin Kudu maso Gabas yayin babban zaben kasar.
Sai dai kuma tsohon dan majalisar ya dage cewa dokar zaman gida na da wani mummunan mataki da koma baya ga ‘yancin dimokradiyyar al’ummar yankin Kudu maso Gabashin kasar nan.
Ya rubuta cewa, “Hukuncin zaman gida da kungiyar IPOB mai fafutuka ta kafa a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya, mataki ne mara kyau da koma baya ga ‘yancin dimokradiyyar al’ummar yankin. Kamata ya yi a yi tir da hakan, a kuma rashin biyayya.”