Hukumar da ke kula da kan iyalar Poland ta ce ‘yan gudun hijira fiye da miliyan biyu da dubu dari bakwai ne suka shiga kasar daga Ukraine, tun da aka soma yakin da Rasha.
Hukumar ta bayyana haka ne ranar Juma’a 15-04-2022.
A makonnin baya bayan nan, ‘yan gudun hijirar da suke tsallakawa zuwa Poland sun ragu sannan masu komawa Ukraine sun karu.
Ranar Alhamis, mutane 26,800 suka tsallaka zuwa Poland, karuwar kashi 8 idan aka kwatanta da ranar Laraba,a cewar hukumar a sakon da ta wallafa a Tuwita. Sai dai hakan ya ragu idan aka kwatanta da mutane 142,300 da suka shiga kasar ranar 6 ga watan Maris.
Mutane 16,800. suke shiga Poland daga Ukraine a kullum kafin a soma yaki.
Sai dai tuni wasu daga cikin ‘yan gudun hijirar suka bar Poland. Amma wani Farfesa a Jami’ar Warsaw da ke bincike kan ‘yan gudun hijira Maciej Duszczyk ya yi kiyasin cewa mutane miliyan 1.2 zuwa miliyan 1.4 suna ci gaba da zama a kasar.