fidelitybank

‘Yan gudun hijira sun shiga tsaka mai wuya a Nasarawa

Date:

Ɗaruruwan ‘yan gudun hijira da ƴaƴansu a Najeriya sun ce sun shiga halin ka-ka-ni-ka-yi bayan hukumomi sun ba su zuwa yau don su tashi, ko kuma a rusa matsugunnansu a jihar Nasarawa.

Hukumomin dai sun tsugunar da ‘yan gudun hijirar kimanin 1,500 a wani sansani cikin garin Lafia tun a 2004 bayan wani rikicin kabilanci da ya tilasta musu tserewa daga jihar Filato.

Hukumomi sun ce suna kokarin tayar da mutanen ne saboda zargin aikata laifuka, amma ‘yan gudun hijirar sun musanta hakan. In ji BBC.

An tsugunar da ‘yan gudun hijirar wadanda suka fito daga Yalwan Shandam na jihar Filato ne, a unguwar Shinge da aka fi sani da unguwar Hijira a yanzu.

Malam Abbas Abdussalam shi ne sakataren kungiyar ‘yan gudun hijirar yace tun da farko da izinin gwamnati suke zaune tun lokacin wurin daji ne kuma yanzu ya zama alkariya hukumomin karamar hukumar Lafiya ke kokarin tayar da su.

Wasu matan masu ƴaƴa da dama sun ce ji suke tamkar yau suka fito gudun hijira.

Shugaban karamar hukumar lafiya Hon. Aminu Mu’azu Maifata ya shaida wa BBC cewa dole ce ta sa za su tashe su, saboda matsalar tsaro.

Kazalika, ya ce sun bai wa ‘yan gudun hijirar notis din su tashi tun-tuni, saboda a cewarsa wurin na karamar hukumar ne.

Bugu da ƙari Honorabul Mai Fata ya ce har wasika suka rubutawa hukumomin jihar Filato ta ofishin sakataren gwamnatin Nasarawa suna shaida musu halin da ake ciki game da ‘yan gudun hijira da suka yi sansani tun 2004.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp