fidelitybank

‘Yan gudun hijira sun shiga tsaka mai wuya a Nasarawa

Date:

Ɗaruruwan ‘yan gudun hijira da ƴaƴansu a Najeriya sun ce sun shiga halin ka-ka-ni-ka-yi bayan hukumomi sun ba su zuwa yau don su tashi, ko kuma a rusa matsugunnansu a jihar Nasarawa.

Hukumomin dai sun tsugunar da ‘yan gudun hijirar kimanin 1,500 a wani sansani cikin garin Lafia tun a 2004 bayan wani rikicin kabilanci da ya tilasta musu tserewa daga jihar Filato.

Hukumomi sun ce suna kokarin tayar da mutanen ne saboda zargin aikata laifuka, amma ‘yan gudun hijirar sun musanta hakan. In ji BBC.

An tsugunar da ‘yan gudun hijirar wadanda suka fito daga Yalwan Shandam na jihar Filato ne, a unguwar Shinge da aka fi sani da unguwar Hijira a yanzu.

Malam Abbas Abdussalam shi ne sakataren kungiyar ‘yan gudun hijirar yace tun da farko da izinin gwamnati suke zaune tun lokacin wurin daji ne kuma yanzu ya zama alkariya hukumomin karamar hukumar Lafiya ke kokarin tayar da su.

Wasu matan masu ƴaƴa da dama sun ce ji suke tamkar yau suka fito gudun hijira.

Shugaban karamar hukumar lafiya Hon. Aminu Mu’azu Maifata ya shaida wa BBC cewa dole ce ta sa za su tashe su, saboda matsalar tsaro.

Kazalika, ya ce sun bai wa ‘yan gudun hijirar notis din su tashi tun-tuni, saboda a cewarsa wurin na karamar hukumar ne.

Bugu da ƙari Honorabul Mai Fata ya ce har wasika suka rubutawa hukumomin jihar Filato ta ofishin sakataren gwamnatin Nasarawa suna shaida musu halin da ake ciki game da ‘yan gudun hijira da suka yi sansani tun 2004.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp