fidelitybank

‘Yan garkuwa sun kashe dan kasuwar Kano duk da karbar kudin fansa

Date:

Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da ke kan hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari sun kashe wani dan kasuwar jihar Kano mai suna Umar Sani, bayan sun karbi kudin fansa a hannun ‘yan uwansa.

Dan kasuwar, an yi garkuwa da shi ne makonni biyu da suka gabata tare da wasu mutane biyar a kan hanyar zuwa Buruku, amma daga baya wasu da suka yi garkuwa da shi suka tabbatar da kashe shi duk da karbar kudin fansa domin a sake su.

Marigayin ya fito ne daga karamar hukumar Fagge a cikin birnin Kano.

Wani dattijo dan uwan marigayin, Hussaini Sani, wanda ya tabbatar wa da Daily Trust rasuwar a ranar Juma’a, ya kuma ce masu garkuwa da mutanen sun sake kiran a ranar Alhamis inda suka bukaci a kara musu Naira miliyan 20 duk da kashe dan kasuwar.

Magaji ya rasu ya bar matarsa ​​da ’ya’yansa hudu, wadanda a halin yanzu suke zaune a karamar hukumar Bichi ta jihar.

Mutuwar tasa na zuwa ne kwanaki 10, bayan gano gawar wani dan kasuwa bayan an biya kudin fansa Naira miliyan 6 ga wadanda suka sace shi a cikin Birnin Gwari.

 

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...
X whatsapp