Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da ke kan hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari sun kashe wani dan kasuwar jihar Kano mai suna Umar Sani, bayan sun karbi kudin fansa a hannun ‘yan uwansa.
Dan kasuwar, an yi garkuwa da shi ne makonni biyu da suka gabata tare da wasu mutane biyar a kan hanyar zuwa Buruku, amma daga baya wasu da suka yi garkuwa da shi suka tabbatar da kashe shi duk da karbar kudin fansa domin a sake su.
Marigayin ya fito ne daga karamar hukumar Fagge a cikin birnin Kano.
Wani dattijo dan uwan marigayin, Hussaini Sani, wanda ya tabbatar wa da Daily Trust rasuwar a ranar Juma’a, ya kuma ce masu garkuwa da mutanen sun sake kiran a ranar Alhamis inda suka bukaci a kara musu Naira miliyan 20 duk da kashe dan kasuwar.
Magaji ya rasu ya bar matarsa da ’ya’yansa hudu, wadanda a halin yanzu suke zaune a karamar hukumar Bichi ta jihar.
Mutuwar tasa na zuwa ne kwanaki 10, bayan gano gawar wani dan kasuwa bayan an biya kudin fansa Naira miliyan 6 ga wadanda suka sace shi a cikin Birnin Gwari.