‘Yan fashin daji sun kashe Mai Garin Mulo na Ƙaramar Hukumar Mashegu ta Jihar Neja, bayan sun yi garkuwa da shi ranar Alhamis.
Rahotanni sun ambato Kwamashinan Harkokin Cikin Gida na Neja Emmanuel Umar na bayyanawa a ranar Juma’a cewa ‘yan bindigar sun afka wa ƙauyen a ranar Alhamis.
Duk da cewa abubuwa sun ɗan lafa a jihar amma har yanzu akan kai hare-hare a Mashegu da Kontagora, in ji shi.
Rahotannin sun ce an sace mai unguwar ne tare da wasu mutum uku.
A jiya Juma’a Gwamnatin Jihar Kaduna mai maƙwabtaka ta ce jami’an tsaro sun kashe ‘yan fashin daji 10 a jihar tare da ƙwace baburan da suke kai hare-hare da su a ƙauyuka.