fidelitybank

‘Yan fashi sun kashe mutane 3 a Jigawa

Date:

Wasu ‘yan fashi da makami a ranar Talata sun kashe mutane uku a karamar hukumar Birninkudu da ke jihar Jigawa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar DSP Lawan Shiisu ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba a Dutse.

“A ranar Talata da misalin karfe 8:00 na dare ne aka samu labari daga kauyen Iggi cewa an hangi wasu ‘yan bindiga uku a kan babur daya a yankin Iyayi na jihar Bauchi, inda suka tunkari kauyen Iggi da ke karamar hukumar Birninkudu ta kauyen Babuwawa.

“Bayan samun labarin, an hada tawagar ‘yan sintiri zuwa yankin, kuma an sanar da duk masu ruwa da tsaki a harkar tsaro, musamman ‘yan banga.

“Da misalin karfe 10:15 na dare ne aka samu kiran tashin hankali daga bangaren Warwade na Birninkudu cewa ‘yan bindigan sun kwace babur daga hannun wani da ba a san ko su wanene ba,” inji shi.

A cewarsa, ‘yan fashin da ake zargin sun yi harbi da dama kan wata mota da ta zo dauke da fasinjoji hudu, inda ya kara da cewa ‘yan fashin sun harbe direban, Hassan Garba daya da fasinjoji biyu, mai suna Garba Maiwake da Shehu Saidu.

Kakakin ya ce an ajiye gawarwakin ne a dakin ajiye gawa na Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya da ke Birninkudu, inda ya kara da cewa rundunar ta zafafa sintiri domin cafke wadanda ake zargi da gudu.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp