Wasu ‘yan fashi sun kaddamarwa da wata motar dakon kudi a unguwar, Idi-Ape da ke Ibadan, babban birnin jihar Oyo.
Jaridar The Nation ta rawaito cewa, wasu majiyoyi sun shaida cewar, ‘yan sanda biyu sun mutu yayin da ‘yan fashin ke harbe-harbe a lokacin da suke gudanar da barnar. Sun ce motar kudin ta fito ne daga daya daga cikin bankunan da ke kusa da inda lamarin ya faru.
A kokarin tabbatar da faruwar lamarin daga ‘yan sanda ya ci tura, domin ba a samu jin ta jami’an hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Oyo ba.
‘Yan fashin sun tafi da motar, amma ba a iya tabbatar da dukkan batutuwan ba, har zuwa lokacin hada wannan rahoto, saboda ba a samu bayanin a hukumance ba. Majiyar ta ce, mazauna garin da masu ababan hawa da ke gefen titi sun buya, domin gudun kada ‘yan fashi da makamin su harbe su.