Rundunar ƴan sandan jihar Kano, ta cafke mutum takwas da ake zargi da yunƙurin kawo tarnaƙi a bikin ƙaddamar da sabbin kwamishinoni da aka yi a baya-bayan nan.
Kakakin rundunar ƴan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, cikin sanarwar da ya wallafa a shafinsa na fesbuk, ya ce an kama mutanen ne da ke bayyana kansu a matsayin magoya bayan ɗaya daga cikin ƴan siyasa da ke neman barazana ga doka da oda.
Kwamishinan ƴan sanda CP Usaini Gumel ya gargarɗi ƴan jagaliya da masu tallafa masu da su guji tayar da zaune tsaye inda ya ce “za a kama duk wani da ke son haifar da barazana ga tsaro da zaman lafiya a wurin da ake gudanar da tarukan gwamnati, sannan zai fuskanci hukuncin abin da ya aikata.”
Sanarwar ta ce mutanen da aka kama a yanzu na sashen binciken manyan laifuka inda ake gudanar da bincike mai zurfi domin hukunta su bisa tanadin doka.
Rundunar ta ce ta ɗauki matakin ne domin tabbatar wa al’ummar jihar cewa ana ɗaukan matakan da suka dace na hana duk wani abu da zai kawo hargitsi da barazanar tsaro a sassan jihar Kano.