fidelitybank

‘Yan daban da suka tayar da rikici a gidan gwamnatin Kano suna hannun ‘yan sanda

Date:

Rundunar ƴan sandan jihar Kano, ta cafke mutum takwas da ake zargi da yunƙurin kawo tarnaƙi a bikin ƙaddamar da sabbin kwamishinoni da aka yi a baya-bayan nan.

Kakakin rundunar ƴan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, cikin sanarwar da ya wallafa a shafinsa na fesbuk, ya ce an kama mutanen ne da ke bayyana kansu a matsayin magoya bayan ɗaya daga cikin ƴan siyasa da ke neman barazana ga doka da oda.

Kwamishinan ƴan sanda CP Usaini Gumel ya gargarɗi ƴan jagaliya da masu tallafa masu da su guji tayar da zaune tsaye inda ya ce “za a kama duk wani da ke son haifar da barazana ga tsaro da zaman lafiya a wurin da ake gudanar da tarukan gwamnati, sannan zai fuskanci hukuncin abin da ya aikata.”

Sanarwar ta ce mutanen da aka kama a yanzu na sashen binciken manyan laifuka inda ake gudanar da bincike mai zurfi domin hukunta su bisa tanadin doka.

Rundunar ta ce ta ɗauki matakin ne domin tabbatar wa al’ummar jihar cewa ana ɗaukan matakan da suka dace na hana duk wani abu da zai kawo hargitsi da barazanar tsaro a sassan jihar Kano.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp