fidelitybank

‘Yan cirani sun daskare a dusar kankara

Date:

Akalla wasu ’yan ci-rani 12 ne da ke kokarin tsallakawa kasashen Turai aka tsinci gawarwakinsu, bayan sun daskare a dusar kankara a kan iyakar kasashen Turkiyya da Girka.

Rahotanni sun nuna cewa, ko sutturar kirki babu a jikin mutanen da aka gano gawarta su.

Ministan Harkokin Cikin Gida na Turkiyya, Suleyman Soylu, ya wallafa hotunan mutanen, a shafin Twitter, shimfide a gefen hanya a kusa da garin Ipsala da ke Arewa maso Yammacin kasar, suna sanye da gajerun wanduna da rigunan T-shirt, duk da sanyin da ake fama da shi.

Ya yi zargin cewa, mutum 12 na daga cikin dimbin wadanda kasar Girkar take yi wa korar kare.

“12 daga cikin ’yan ci-rani 22 da Girka ta kora sun daskare a dusar kankara sannan suka mutu, bayan an cire musu sutturarsu da takalma,” inji Ministan.

Tsananin sanyi dai a yankin ya kai kusan tsakanin digiri biyu zuwa uku a ma’aunin celcius da daddare a karshen watan Janairu da kuma farkon Fabrairu.

Minista Suleyman ya zargi masu tsaron iyakar na Girka da nuna rashin imani a kan mutanen, inda ya kuma ce Tarayyar Turai na da rauni matuka.

Ita kuwa a nata bangaren, kasar Girka, ta bakin Ministan Shige da Fice na kasar, Notis Mitarachi, ta bayyana lamarin a matsayin babbar masifa, amma ta zargi Turkiyya da siyasantar da lamarin.

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Majalisar Dinkin Duniya (IOM) dai ta ce ita ma ta kadu matuka da jin labarin mutuwar mutanen.

Wani rahoto da Hukumar Kula na ’Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ya kiyasta cewa sama da mutum 2,500 ne ko dai suka mutu ko kuma suka bace a kokarinsu na tsallakawa Turai daga Arewacin Afirka da Turkiyya a shekarar 2021 kawai. A cewar Aminiya.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp