fidelitybank

‘Yan cirani sun daskare a dusar kankara

Date:

Akalla wasu ’yan ci-rani 12 ne da ke kokarin tsallakawa kasashen Turai aka tsinci gawarwakinsu, bayan sun daskare a dusar kankara a kan iyakar kasashen Turkiyya da Girka.

Rahotanni sun nuna cewa, ko sutturar kirki babu a jikin mutanen da aka gano gawarta su.

Ministan Harkokin Cikin Gida na Turkiyya, Suleyman Soylu, ya wallafa hotunan mutanen, a shafin Twitter, shimfide a gefen hanya a kusa da garin Ipsala da ke Arewa maso Yammacin kasar, suna sanye da gajerun wanduna da rigunan T-shirt, duk da sanyin da ake fama da shi.

Ya yi zargin cewa, mutum 12 na daga cikin dimbin wadanda kasar Girkar take yi wa korar kare.

“12 daga cikin ’yan ci-rani 22 da Girka ta kora sun daskare a dusar kankara sannan suka mutu, bayan an cire musu sutturarsu da takalma,” inji Ministan.

Tsananin sanyi dai a yankin ya kai kusan tsakanin digiri biyu zuwa uku a ma’aunin celcius da daddare a karshen watan Janairu da kuma farkon Fabrairu.

Minista Suleyman ya zargi masu tsaron iyakar na Girka da nuna rashin imani a kan mutanen, inda ya kuma ce Tarayyar Turai na da rauni matuka.

Ita kuwa a nata bangaren, kasar Girka, ta bakin Ministan Shige da Fice na kasar, Notis Mitarachi, ta bayyana lamarin a matsayin babbar masifa, amma ta zargi Turkiyya da siyasantar da lamarin.

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Majalisar Dinkin Duniya (IOM) dai ta ce ita ma ta kadu matuka da jin labarin mutuwar mutanen.

Wani rahoto da Hukumar Kula na ’Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ya kiyasta cewa sama da mutum 2,500 ne ko dai suka mutu ko kuma suka bace a kokarinsu na tsallakawa Turai daga Arewacin Afirka da Turkiyya a shekarar 2021 kawai. A cewar Aminiya.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp