fidelitybank

‘Yan China 7 sun shaki iskar ‘yanci a Neja

Date:

Gwamnatin jihar Neja ta sanar da sakin wasu ‘yan kasar China 7 da aka yi garkuwa da su a unguwar Ajata-Aboki da ke karamar hukumar Shiroro a jihar.

Wadanda abin ya shafa, wadanda aka samu ‘yancinsu ta hanyar aikin ceto da rundunar sojin saman Najeriya, NAF ta yi, an sace su ne a watan Yunin 2022.

Gwamnatin ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kwamishinan tsaro na cikin gida da ayyukan jin kai, Hon. Emmanuel Bagna Umar in Minna.

A cewarsa, “muna samun rahotannin farin ciki matuka game da aikin ceto da NAF ta yi wajen ceto ‘yan kasar China 7 da aka yi garkuwa da su. Mai Girma Gwamna Abubakar Sani Bello, ya yabawa kwazon kwamandan da sojojin runduna ta 271 NAF Detachment na wannan gagarumin aikin.

“Musamman ya yaba da salon jagoranci da basirar hafsan hafsan sojin sama, Air Marshal Oladayo Amao, wanda a karkashin jagorancin NAF ta ci gaba da samun gagarumar nasara a ayyukanta a fadin kasar, ciki har da nasarar ceto wadannan ‘yan kasar China a Kampanin Doka, Gwaska area of Birnin Gwari LGA, Kaduna State”.

Ya kuma bayyana cewa gwamnatin Neja a karkashin jagorancin Gwamna Sani Bello za ta ci gaba da hada kai da duk jami’an tsaro a jihar domin tabbatar da ‘yan kasa suna cikin koshin lafiya.

Umar ya kara da cewa, “Gwamna Bello yana taya wadanda abin ya shafa, iyalansu, abokansu da abokan huldar su domin ceto su da kuma yi musu fatan alheri”.

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp