Shalkwatar sojoji ta kasa, ta sanar da mika wuya ga daruruwan ‘yan Boko Haram, da mayakan kungiyar IS da ke yammacin Afirka (ISWAP).
Rundunar sojin ta bayyana ta shafinta na Twitter a daren Laraba cewa, jimillar ‘yan ta’adda dari uku da sha hudu ne suka mika kansu ga sojoji a wani samame da suka kai a karamar hukumar Bama ta jihar.
Sojojin sun kuma ceto manoma goma sha biyu daga hannun ‘yan ta’addan.
Tsoffin mayakan a cewar shelkwatar sojojin a halin yanzu ana bayyana sunayensu.
“A ci gaba da kai hare-hare kan ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas ya sake samun nasara a yau, 29 ga watan Yuni, 2022 yayin da mayakan Boko Haram/ISWAP 314 suka mika wuya ga sojoji a karamar hukumar Bama ta jihar Borno. Bugu da kari, sojoji sun kuma ceto manoma 12.
“Ana ci gaba da bayyana bayanan ‘yan ta’addan da suka mika wuya.”