Ƴan bindiga sun yi wa garin Ƴangeme ƙawanya dake Karamar Hukumar Kanƙara.
Ƴan ta’addan dai, ɗauke da muggan makamai Sun shiga ƙauyen ne, bayan an yi Sallar Isha’i, inda suka cigaba da harbe-harbe a saman iska, domin tsoratar da Al’ummar garin.
Jaridar Katsina Post ta tabbatar da faruwar lamarin cewa, lamarin ya faru ne bayan ƴan bindigar sun shiga garin.
Wannan na zuwa ne kwana ɗaya dakai hari a wani ƙauye da ake kira Gidan Mai Ruwa, inda suka kashe mutum ɗaya, tare da tafiya da shanun sa dana mutane, gami da Jikkata wasu.