A daren Laraba ne wasu ‘yan bindiga dauke da makamai suka kai hari a unguwar Mai Bakko da ke Kudancin Katsina, inda suka kashe mutum daya tare da yin garkuwa da wasu da suka hada da mata da kananan yara.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da wani mai sharhi kan harkokin tsaro, Bakatsine, ya fitar a shafinsa na X ranar Alhamis.
Bakatsine, ya nuna damuwarsa kan karuwar hare-hare a Kudancin Katsina bayan yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan bindiga a jihar Kaduna.
“A jiya da daddare ‘yan bindiga sun kai hari a unguwar Mai Bakko, inda suka kashe mutum daya tare da yin garkuwa da mutane da dama a unguwar da suka hada da yara da mata.
“Abin takaici ne yadda hare-haren ‘yan bindiga ke karuwa a Kudancin Katsina bayan yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan bindiga a jihar Kaduna,” in ji Bakatsine.