fidelitybank

‘Yan Bindiga sun yi garkuwa tare da kashe wani a Katsina

Date:

A daren Laraba ne wasu ‘yan bindiga dauke da makamai suka kai hari a unguwar Mai Bakko da ke Kudancin Katsina, inda suka kashe mutum daya tare da yin garkuwa da wasu da suka hada da mata da kananan yara.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da wani mai sharhi kan harkokin tsaro, Bakatsine, ya fitar a shafinsa na X ranar Alhamis.

Bakatsine, ya nuna damuwarsa kan karuwar hare-hare a Kudancin Katsina bayan yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan bindiga a jihar Kaduna.

“A jiya da daddare ‘yan bindiga sun kai hari a unguwar Mai Bakko, inda suka kashe mutum daya tare da yin garkuwa da mutane da dama a unguwar da suka hada da yara da mata.

“Abin takaici ne yadda hare-haren ‘yan bindiga ke karuwa a Kudancin Katsina bayan yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan bindiga a jihar Kaduna,” in ji Bakatsine.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp