fidelitybank

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane kusan 46 a Katsina

Date:

Wasu ‘yan bindiga a kauyukan Batsari da Funtua a jihar Katsina sun yi garkuwa da mutane kusan 46 a karshen mako.

Wata majiya ta shaida wa DAILY POST cewa a kauyen Karare da ke karamar hukumar Batsari a ranar Juma’a, an kashe mutum daya, yayin da aka yi garkuwa da mutane 28.

Ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyen ne da safe inda suka tafi da wadanda lamarin ya rutsa da su, ciki har da mata da kananan yara kimanin 40 suna hawan babura.

A cewar majiyar, an yi garkuwa da daliban kauyen Kokiya da ke kan hanyar zuwa makarantar sakandare ta gwamnati ta Karare.

Ya kara da cewa, ‘yan bindigar sun fito ne daga yankin kudancin kauyen inda suka fara harbe-harbe kai-tsaye, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum daya.

Majiyar ta ce barayin sun yi awon gaba da mutane 28 da suka hada da dalibai, amma daga baya sun sako hudu daga cikinsu, inda suka jaddada cewa wadanda aka sako sun hada da Malam Ladan daya da yara uku a yayin da suka aike musu da sakon cewa ba za su karbi kudin tsohon naira ba.

A cewarsa, wani mutum daya ya tsere, yayin da a halin yanzu mutane 23 ke tare da ‘yan bindigar kuma babu wata bukatar kudin fansa da masu garkuwan suka yi.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...

Ambaliyar ruwa ta kashe mutuane takwas a Ebonyi

Ambaliya, wadda mamakon ruwan sama ya janyo, ta yi...

Bankin Duniya zai kashe wa yankin Arewa a Najeriya dala miliyan 300

Bankin Duniya ya amince da kasafin kuɗi dala miliyan...

Giyar mulki na kwasar Trump – ‘Yan Majalisar Democrat

'Yan Democrats a Amurka sun zargi Donald Trump da...

Kama Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi ba daidai ba ne – PDP

Jam'iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da...

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...
X whatsapp