Kimanin mutane 1,789 ne ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Kaduna cikin watanni shida a wannan shekarar, kamar yadda jihar ta bayyana.
Da yake gabatar da rahoton yanayin tsaro na shekarar 2022 ga gwamnatin jihar a ranar Juma’a, kwamishinan ma’aikatar tsaron cikin gida da harkokin cikin gida ta jihar, Samuel Aruwan, ya bayyana cewa a cikin wannan lokaci an kashe ‘yan bindiga 161 a garuruwa daban-daban da jami’an tsaro suka ci karo da su.
A cewar kwamishinan, jami’an tsaro a wurare daban-daban a zango na biyu sun kashe ‘yan bindiga 59.
A daidai wannan lokacin da ake bitar, ya bayyana cewa an kashe mutane 285 a sanadiyar ‘yan fashi, rikicin kabilanci da kuma ramuwar gayya.
A cikin kwata na uku, Aruwan ya kara da cewa an yi garkuwa da mutane 804, inda 508 daga cikin adadin aka samu a yankin Kaduna ta tsakiya daga ranar 1 ga Yuli zuwa Satumba, 2022.
A cewarsa, “Satun shanu 1,133 ne, yayin da aka kashe ‘yan bindiga 109 a lokacin da suke yin mu’amala da sojojin kasa.”
Ya kara da cewa an kama mutane 654 da ake zargi a lokacin da ake binciken.