fidelitybank

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da matafiya a hanyar Zamfara zuwa Funtua

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan ta’adda ne, sun kai wani samame a kan hanyar Zamfara zuwa Funtua, inda suka yi garkuwa da dimbin matafiya da ke tafiya zuwa wurare daban-daban na kasar nan.

A cewar wani ganau, Mista Nura Ola Tsafe, ‘yan ta’addan sun gudanar da samamen ne a ranakun Juma’a da Asabar a wurare daban-daban da ke tsakanin Gusau- Gidan Dawa-Yandoto Daji a karamar hukumar Tsafe.

Ya ce an fara gudanar da ayyukan ne a ranar Juma’a, kuma ‘yan bindigar sun ci gaba da munanan ayyukansu har zuwa ranar Asabar, inda ya ce an kai wadanda aka sace zuwa dajin.

Karanta Wannan: Zamfara ta kori kungiyoyi masu zaman kansu daga jihar

“Shahararrun ‘yan bindigar sun yi awon gaba da fasinjojin da ba su ji ba ba su gani ba a hanyarsu ta zuwa halartar Mauludin Musulunci. ‘Yan ta’addan sun yi garkuwa da wasu fasinjojin motocin kasuwanci guda biyu a tsakanin Yandoton Daji da Kwatarkwashi,” inji shi.

Ya kuma kara da cewa ‘yan bindigan sun kuma kai wa wasu mazauna garin Tsafe hari a ranar Juma’a a kan Yandoton Daji-Gidan Dawa, inda ya kara da cewa wadanda harin ya rutsa da su sun tsere da kyar ne sakamakon shiga tsakani da sojojin suka yi.

Nura Tsafe ya koka da yadda irin wadannan ayyuka a kan titin Gusau zuwa Funtua ya zama abin damuwa musamman a yanzu da al’ummar kasar ke shirin tunkarar babban zabe na 2023.

Idan dai za a iya tunawa, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Kolo Yusuf tare da tawagarsa ta ‘yan Tactical, sun gudanar da wani samame a kan hanyar Zamfara zuwa Funtua domin kara tabbatar da tsaro a hanyar da kuma karfafa kwarin gwiwar matafiya.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp