Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan ta’adda ne, sun kai wani samame a kan hanyar Zamfara zuwa Funtua, inda suka yi garkuwa da dimbin matafiya da ke tafiya zuwa wurare daban-daban na kasar nan.
A cewar wani ganau, Mista Nura Ola Tsafe, ‘yan ta’addan sun gudanar da samamen ne a ranakun Juma’a da Asabar a wurare daban-daban da ke tsakanin Gusau- Gidan Dawa-Yandoto Daji a karamar hukumar Tsafe.
Ya ce an fara gudanar da ayyukan ne a ranar Juma’a, kuma ‘yan bindigar sun ci gaba da munanan ayyukansu har zuwa ranar Asabar, inda ya ce an kai wadanda aka sace zuwa dajin.
Karanta Wannan: Zamfara ta kori kungiyoyi masu zaman kansu daga jihar
“Shahararrun ‘yan bindigar sun yi awon gaba da fasinjojin da ba su ji ba ba su gani ba a hanyarsu ta zuwa halartar Mauludin Musulunci. ‘Yan ta’addan sun yi garkuwa da wasu fasinjojin motocin kasuwanci guda biyu a tsakanin Yandoton Daji da Kwatarkwashi,” inji shi.
Ya kuma kara da cewa ‘yan bindigan sun kuma kai wa wasu mazauna garin Tsafe hari a ranar Juma’a a kan Yandoton Daji-Gidan Dawa, inda ya kara da cewa wadanda harin ya rutsa da su sun tsere da kyar ne sakamakon shiga tsakani da sojojin suka yi.
Nura Tsafe ya koka da yadda irin wadannan ayyuka a kan titin Gusau zuwa Funtua ya zama abin damuwa musamman a yanzu da al’ummar kasar ke shirin tunkarar babban zabe na 2023.
Idan dai za a iya tunawa, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Kolo Yusuf tare da tawagarsa ta ‘yan Tactical, sun gudanar da wani samame a kan hanyar Zamfara zuwa Funtua domin kara tabbatar da tsaro a hanyar da kuma karfafa kwarin gwiwar matafiya.