‘Yan bindiga sun yi awon gaba da wani jamiāin Kwastam a karamar hukumar tsafe da ke jihar Zamfara.
A yanzu haka sun kira iyalan jami’in mai suna Muhammad Hassan Lawal, inda suka bukaci su biya Naira miliyan 10 a matsayin kudin fansa.
Rohatanni na nuni da cewa, maharan sun yi garkuwa da wasu mata shida a yankin a ranar Lahadi, 13 ga watan Fabrairu.
An yi garkuwa da jamiāin kwastam din mai kula da jihohin Kano da Jigawa, Muhammad Hassan Lawal wanda ya ziyarci iyalinsa a daren ranar Jumaāa, 11 ga watan Fabrairu.
A cewar Hassan Tsafe, wani mazaunin kauyen da abun ya faru kan idon sa, maharan sun shafe kimanin mintuna 30 kafin sojojin da aka kira suka iso.