fidelitybank

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da daraktan ma’aikatan kudi na Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da Malam Sabiu, darakta a ma’aikatar kudi ta jihar Zamfara tare da matarsa da ‘ya’yansa biyu.

Lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Talata a rukunin gidajen Damba da ke Gusau, babban birnin jihar.

A cewar wani ganau, wani mazaunin unguwar, Auwalu Garba, ya ce, ‘yan bindigar sun shiga gidan Sabiu ne da misalin karfe 1:30 na daer.

Ya kara da cewa ‘yan bindigar sun shiga gidan da manyan makamai inda suka nufi gidan Sabiu.

“Lokacin da suka isa unguwarmu, ba su yi harbi ba, kuma ba su shiga wani gida ba.

“Sai kawai suka je gidan Sabiu inda suka karya kofa, suka shiga dakin kwana suka yi awon gaba da shi da matarsa.

“Daga baya sun koma wani daki suka sace yara biyu sannan suka koma daji.”

Garba ya ce barayin sun sako matar Sabiu saboda rashin lafiya da suka yi garkuwa da su.

Kokarin samun bayanai daga kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Yazid Abubakar, ya ci tura, domin an kasa samunsa ta hanyar wayarsa.

Gidajen Damba da ke garin Gusau, babban birnin jihar Zamfara, sun kasance wuraren da ‘yan bindiga ke kai hare-hare a ‘yan shekarun nan.

Al’ummar yankin dai sun sha fuskantar matsalar sace-sacen mutane da dama, lamarin da ya sa mazauna yankin kaura zuwa wuraren da babu tsaro saboda fargaba.

A watan Fabrairun 2022, an samu irin wannan harin inda ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da matar da ‘ya’yan wani Daraktan kudi a ma’aikatar kudi ta jihar Zamfara, Sirajo Hassan.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp