fidelitybank

‘Yan bindiga sun yi awon gaba da mazaunin Tambuwal

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da Aliyu Maidamma, kane ga marigayi dan kasuwa, Alhaji Dikko Chemist.

Rahotanni sun ce an yi garkuwa da shi ne bayan harbe-harben bindiga da aka yi a garin Tambuwal, hedikwatar karamar hukumar Tambuwal a jihar Sokoto.

An ce ‘yan bindigar da ake zargin sun kai harin ne bayan da jami’an tsaro suka kashe abokan aikinsu a yankin Kebbe mai tazarar kilomita 45 daga Tambuwal.

Sojojin sun yi sansani a garin Kebbe, hedikwatar karamar hukumar Kebbe, wanda ke daya daga cikin lungunan jihar.

Wata majiya daga garin Tambuwal ta bayyana cewa ‘yan bindigar sun far wa tashar motar Tambuwal da misalin karfe 9 na dare a adadinsu, inda suka yi ta harbe-harbe, kafin su yi garkuwa da Maidamma.

Ya kara da cewa wadanda suka gansu sun ce sun nufi garin Kebbe.

Majiyar ta ce, “Babu haske a Tambuwal lokacin da aka kai harin, wanda hakan ya bai wa ‘yan bindiga damar kai harin cikin nasara ba tare da turjiya ba.

Kiraye-kirayen da aka yi wa mataimakin Sufeton ‘yan sanda, Ahamed Rufa’e, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar bai ci gaba da gudana ba.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp