Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne a ranar Larabar da ta gabata, sun tare hanyar Kachia a kauyen Tashan-Iche, karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna tare da yin garkuwa da wasu matafiya.
Daya daga cikin matafiyan da suka tsere da kyar, Mista Shuaibu Eneojo ya shaidawa manema labarai a Kaduna a ranar Larabar da ta gabata cewa ‘yan bindigar sun far wa masu ababen hawa da misalin karfe 7:00 na safe inda suka yi awon gaba da wasu mutane da ke kan hanyar a lokacin.
Ya yi zargin cewa galibin ma’aikatan da ke zuwa Kajuru, sun koma gida ne biyo bayan toshewar hanyar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Kaduna, DSP Mohammed Jalige, bai tabbatar da faruwar harin ba.