fidelitybank

‘Yan bindiga sun sako mutane 74 daga cikin 85 a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bindiga da suka yi garkuwa da mutane 85 a kauyen Wanzamai da ke karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara sun sako mutane 74.

Daya daga cikin mazauna yankin Usman Mohammed ya shaidawa DAILY POST cewa, an sako mutanen 74 a daren ranar Juma’ar da ta gabata, ya kara da cewa sauran mutane 11 da suka rage na hannunsu.

“Mun yi farin ciki da cewa ‘yan bindigan sun sako mutane 74 a daren Juma’a daga cikin 85 da suka yi garkuwa da su amma har yanzu ba mu ji dadi ba saboda sauran 11 da ‘yan fashin ke tsare da su.

“Ba mu ga sauran mutane 11 ba kuma ba mu san abin da ya same su ba.

“Ko da ‘yan ta’addan sun tara karin kudi Naira miliyan 3 da suka yi alkawarin sakin mutanen mu, kuma a yanzu sun sako mutane 74 da aka kashe.

“‘Yan ta’addan ba su sanar da mu ko sauran mutane 11 suna raye ko a’a ba,” in ji shi.

A cewarsa, wasu daga cikin wadanda aka sako a halin yanzu suna asibitocin Wanzamai da Yankara suna karbar magani, yayin da wasu kuma suna gidajensu daban-daban.

Jaridar DAILY POST ta ruwaito cewa, har yanzu gwamnatin jihar da rundunar ‘yan sanda ba su fitar da sanarwa kan sakin wadanda lamarin ya rutsa da su ba.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp