fidelitybank

‘Yan Bindiga sun sake kashe mutane 40 a Filato

Date:

Aƙalla mutum 40 ne aka sake kashewa a wani hari da wasu mahara suka kai a garin Zike da ke yankin Kwall a ƙaramar hukumar Bassa ta jihar Filato.

Mai bai wa gwamnan jihar Filato shawara kan harkokin tsaro Admiral Shipi Gakji mai ritaya ya tabbatar wa BBC cewa an kai harin ne a cikin dare, wayewar garin yau Litinin.

Bayanai sun nuna cewa maharan sun buɗe wuta kan mai uwa da wabi a lokacin da suka shiga ƙauyen.

Gakji ya shaida wa BBC cewa “E haka ne, an kai harin, muna ƙoƙarin haɗa yawan mutanen da aka kashe, amma tabbas yawan ya kai haka ɗin (40).”

Wannan na zuwa ne kimanin mako ɗaya bayan wani hari da ƴan bindiga suka kai a ƙaramar hukumar Bokkos ta jihar ta Filato, wanda ya yi sanadin kashe fiye da mutum 50 da tarwatsa wasu da dama.

Filato jiha ce mai al’umma masu mabambantan ƙabila da addini, wadda ta daɗe tana fama da rikici mai nasaba da addini da kuma ƙabilanci.

Sau da yawa akan zargi makiyaya da laifin kai irin waɗannan hare-hare, sai dai a lokuta da dama sukan musanta hakan.

Hukumomi a baya sun sha kafa kwamitoci domin magance matsalar, amma duk da haka, lamarin ya ci tura.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp