Wasu ƴan bindiga sun sace jigo kuma sakataren jam’iyyar APC a karamar hukumar Ikwerre ta jihar Rivers, Mista Amadi Osaronu.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa bayanai sun nuna wasu mutane ne sanye da kaya irin na ‘yan sanda dauke da bindigogi suka yi awon-gaba da Osaronu daga gidansa da ke Aluu, a yankin karamar hukumar ta Ikwerre a jiya Laraba.
Sakataren yada labarai na jam’iyyar ta APC a jihar ta Rivers ya tabbatar da lamarin lokacin da jaridar ta tuntube shi.
Karanta Wannan: PDP ta na kokarin yin kutse cikin rumbin INEC a Kwara – APC
Yana mai cewa, ‘’babu wata tursasawa ko neman harzuka su da za a yi da zai canja sakamakon zaben 18 ga watan Maris, wanda za a doke PDP,’’
Wannan dai na kasancewa ne yayin da ake shirin gudanar da zaben gwamnoni da ‘yan majalisar dokoki a jihohi 28 daga cikin 36 na Najeriya.