Akalla mutane 30 ne aka ce an sace wasu masu ibada yayin da suke sallah a wani masallaci a garin Tsafe hedikwatar karamar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara.
Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne a safiyar ranar Alhamis a lokacin da ‘yan ta’addan suka mamaye wurin a lokacin da masu ibada ke gudanar da sallar asuba.
Wakilinmu ya tattaro mana cewa maharan da suka addabi yankin, sun mamaye masallacin, inda suka rika harbe-harbe da nagartattun muggan makamai kafin daga bisani suka shiga dajin, wanda ba a tantance yawan su ba,
Rundunar ‘yan sandan jihar ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoton, yayin da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Yazid Abubakar bai amsa kiransa ba.