Wasu ‘yan bindiga sun sace mahaifiyar shugaban Marasa Rinjaye a Majalisar dokokin Jihar Kano, Isiyaku Ali Danja da tsakar daren Laraba.
Maharan sun shiga gidan, Hajiya Zainab da ke karamar hukumar Gezawa da misalin ƙarfe 1:00 na dare ɗauke da makamai, inda su ka tilasta wa mutan gidan cewa sai an kai su ɗakinta.
Saminu Danja wanda ɗa ne ga ɗan majalisar, ya faɗa wa BBC cewa ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton ɓarayin ba su tuntuɓe su ba.
Honorabul Isiyaku Ali Ɗanja, shi ne tsohon Kakakin Majalisar Kano kuma wakilin Gezawa a majalisar.
Yankin Arewa maso Yammacin Najeriya na ci gaba da fuskantar sace-sacen mutane, domin neman kuɗin fansa, sai dai lamarin bai yi ƙamari a Kano ba kamar jihohi maƙotanta.