fidelitybank

‘Yan bindiga sun sace daliban makarantar tsangaya a Sokoto

Date:

Wasu ‘yan bindiya dauke da makamai sun kai hari kauyen Gidan Bakuso da ke yankin karamar hukumar Gada a jihar Sokoto, tare da sace daliban wata tsangaya.

Rahotonni na cewa maharan sun far wa garin ne da tsakar daren ranar Juma’a lokacin da daliban ke barci.

Dan majalisar tarayyar mai wakiltar yankin, Honarabul Bashir Usman Gorou ya tabbatar wa BBC faruwar harin, inda ya ce kimanin dalibai 15 ne ‘yan bindigar suka sace, da wasu mata hudu.

Ya ce daliban almajirai ne na makarantar Allo wadanda shekarun suka kama daga takwas zuwa 14.

Baya ga daliban tsangayar, dan majalisar ya ce a yanzu haka akwai fiye da mutum 63 a yankin da ke hannun ‘yan bindiga, to amma wannan shi ne karo na farko da ake sace kananan almajirai a yankin.

Harin dai na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin jihar ke kaddamar da jami’an sa kai na tsaro don magance matsalar tsaron a jihar.

A baya-bayan nan ‘yan bindiga sun zafafa kai hare-hare tare da sace mutane masu yawa a wasu yankunan arewacin Najeriya.

Ko a ranar Alhamis da ta gabata ma wasu ‘yan bindiga dauke da makamai suka kai hari makarantar furame da karamar sakandiren Kuriga a jihar Kaduna, tare da sace daliban makarantar kimanin 287.

Haka ma makon da ya gabata wasu mahara suka sace wasu mutane mazauna sansanin ‘yan gudun hijira fiye da 100 galibinsu mata da kananan yara a lokacin da suke neman itacen girki a garin Gambouro Ngala a jihar Borno da ke yankin arewa maso gabashin kasar

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp