fidelitybank

‘Yan bindiga sun sace daliban jami’ar kimiya da fasaha ta Okene dake Kogi

Date:

A ranar Alhamis da daddare ne ƴan bindiga suka mamaye jami’ar kimiyya da fasaha ta Confluence da ke Okene a jihar Kogi inda suka sace wasu ɗalibai.

Wani shaida ya ce ƴan bindiga sun kutsa jami’ar cikin dare yayin da wasu ɗalibai ke karatu domin shiryawa jarrabawar da ke tafe.

Majiyar ta ce ƴan bindigar sun shiga jami’ar ne ta daji inda suka shiga ɗakunan karatu uku tare da buɗe wuta.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, ya ce majiyar ta bayyana cewa ƴan bindigar sun tsare ɗaliban a ajujuwansu inda suka riƙa ɗibansu, “an jefa makarantar cikin ruɗani yayin da ɗalibai cikin fargaba a wasu ajujuwan suka nemi mafaka, suka kuma watsu zuwa wasu wuraren jami’ar.”

A cewar majiyar, ɗaliban na shiryawa jarabawar zango na farko da za a soma ranar 13 ga watan Mayu, lokacin da ƴan bindigar suka afka masu.

Shugaban jami’ar, Farfesa Abdulrahman Asipita, ya tbbatar da faruwar lamarin sai dai bai ce komai ba game da adadin ɗaliban da ƴan bindigar suka yi garkuwa da su.

Ƙoƙarin ji daga kwamishinan ƴan sandan Kogi, Mista Bethrand Onuoha, bai yi nasara ba.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp