fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe ‘yan sanda uku a Neja

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba sun kashe jami’an ‘yan sandan uku a jihar Neja.

Jami’an tsaro sun yi wannan kiran ne a lokacin da suke amsa kiran gaggawa a ranar Alhamis, 12 ga watan Mayu, kamar yadda kafar yada labarai ta Naija ta ruwaito.

Da yake bada rahoton lamarin, Aminiya ta tabbatar da cewa maharan da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, sun bindige jami’an ‘yan sanda uku da wani direban babur ne a Suleja a ranar Alhamis da misalin karfe 11 na dare.

Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi wa jami’an tsaron kwanton bauna ne da watakila suna jiran jami’an tsaro a kusa da wani wuri da ake kira Old Barrack.

An bayyana sunayen jami’an da aka kashe kamar haka; SGG Hosea Saba, CPL Yahaya Yakubu da PSC Aminu Sani, dukkansu ma’aikatan B Division Suleja ne.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Shugaban Majalisar Suleja, Abdullahi Shuaibu Maje, ya ce kimanin mutane uku ne suka tsira daga harin, ciki har da dan banga.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp